Wane mataki Najeriya ke ciki wajen aiwatar da kasafin kuɗin 2026?
Wata Cibiyar da ke Neman Tabbatar da Adalcin Ga Jama'a (CSJ) ta buƙaci Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta fara aiwatar da kasafin kuɗin manyan ayyuka na shekarar 2026 nan take, tana mai gargaɗin cewa ci gaba da jinkirta hakan ya saɓa wa tanade-tanaden kundin tsarin mulki da dokar kula da kuɗaɗen Jama'a da kuma dokar kasafin kuɗi.